Gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa a Najeriya - podcast episode cover

Gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa a Najeriya

Nov 18, 202410 min
--:--
--:--
Listen in podcast apps:
Metacast
Spotify
Youtube
RSS

Episode description

Shirin Duniyar Wasanni a wannan makon ya yi duba ne kan irin gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa wajen zakulo matasan ƴan wasa da horar da su a Nigeria. Wannan dai wani bangare ne na gudummawarsu ga ci gaban wasan kwallon ƙafa a Nigeria, tsofin ƴan wasan tawagar Super Eagles na ƙasar, sun fara kafa cibiyoyi masu zaman kan su, da su ke zakulowa tare da horar da matasa don yin fice a harkar ta kwallon kafa.

Irin wadannan cibiyoyin horar da matasa wasan na kwallon kafa da a turance ake kira Football Academy, kan shiga birane da karkara don tuntubar ƙanana da matsakaitan club-club, domin samun ƴan wasan daga wajen su da za a yi rijistarsu a wannan cibiya.

Pascal Patrick, tsohon ɗan wasan Super Eagles kuma shugaban Hukumar kwallon kafa ta NFA a jihar Bauchi kana co-odinetan tawagar Super Eagles na Nigeria, na daya daga cikin tsofaffin ƴan wasan ƙasar da suka kafa irin wannan cibiya a jihar Bauchi.

Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Khamis Saleh.......

For the best experience, listen in Metacast app for iOS or Android
Open in Metacast
Gudummawar da cibiyoyin horar da matasa wasan kwallon ƙafa ke bayarwa a Najeriya | Wasanni podcast - Listen or read transcript on Metacast