Yadda ‘Yan Arewa Za Su Samu Kuɗi A Soshiyal Midiya
Feb 07, 2024•26 min
Episode description
Kafafen sada zumunta sun zama farfajiyar baje kolin basira, yayin da ta kan zame musu hanyar bayyana damuwa da share kokensu.
Ana yawan buga misali da cewa an yiwa yankin Arewacin Najeriya nisa wajen samun tagomashin a soshiyal midiya.
Shirin Daga Laraba na wannan mako ya duba dabarun da masu amfani da shafukan za su bi wajen ganin sun amfana yadda ya kamata.
For the best experience, listen in Metacast app for iOS or Android
