Me Nasarar Da John Mahama Ya Samu Ke Nufi Ga kasar Ghana
Dec 11, 2024•30 min
Episode description
A karshe dai an ayyana John Mahama a matsayin zababben shugaban kasar Ghana bayan da al’ummar kasar sun yanke shawarar zabensa lokacin da suka kada kuri’a ranar Asabar din da ta gabata.
Duk da sauran ‘yan Takara da John Mahama ya kara da su, ciki harda mataimakin shugaban kasar mai ci a yanzu wato Mahamudu Bawumia Musulmi na farko da ya tsaya takarar shugabancin kasar.
Shirin Daga Laraba na wannan makon zaiyi Nazari ne kan nasarar da John Mahama ya samu a zaben kasar Ghna da kuma kalubalen da zai iya fuskanta a shekara daya na farkon wa’adin sa.
For the best experience, listen in Metacast app for iOS or Android
